Littafi Mai Tsarki

Zab 102:16-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Sa'ad da Ubangiji ya sāke gina SihiyonaZai bayyana girmansa.

17. Zai saurari jama'arsa wadda ya rabu da ita,Zai kuwa ji addu'arta.

18. Ku rubuta abin da Ubangiji ya aikata don zamani mai zuwa,Don waɗanda ba a haife su ba tukuna,Su ma su yabe shi.

19. Ubangiji ya duba ƙasaDaga Sama, tsattsarkan wurinsa,Daga Sama ya dubi duniya,