Littafi Mai Tsarki

Mar 7:27-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Yesu ya ce mata, “Bari 'ya'ya su ƙoshi tukuna, domin bai kyautu a bai wa karnuka abincinsu ba.”

28. Amma ta amsa masa ta ce, “I, haka ne, ya Ubangiji, amma ai, karnuka sukan ci suɗin 'ya'ya.”

29. Sai ya ce mata, “Saboda wannan magana taki, koma gida, aljanin, ai, ya rabu da 'yarki.”

30. Sai ta koma gida ta iske yarinyar a kwance a gado, aljanin kuwa ya fita.

31. Sai ya komo daga wajen Taya, ya bi ta Sidon ya je Tekun Galili ta Dikafolis.

32. Suka kawo masa wani kurma mai i'ina, suka roƙe shi ya ɗora masa hannu.