Littafi Mai Tsarki

Mar 16:10-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ita kuwa ta tafi ta faɗa wa waɗanda dā suke tare da shi, ta tarar suna baƙin ciki, suna kuka.

11. Amma da suka ji yana da rai, har ma ta gan shi, sai suka ƙi gaskatawa.

12. Bayan haka ya bayyana da wata kama ga waɗansu biyu daga cikinsu, sa'ad da suke tafiya ƙauye.

13. Suka koma suka gaya wa sauran, su ma kuwa ba su gaskata su ba.

14. Daga baya ya bayyana ga sha ɗayan nan, su kansu, sa'ad da suke cin abinci. Sai ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu da taurinkansu, domin ba su gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi ba.

15. Sai ya ce musu, “Ku tafi ko'ina a duniya, ku yi wa dukkan 'yan adam bishara.