Littafi Mai Tsarki

Mar 10:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Yesu ya tashi daga nan, ya tafi ƙasar Yahudiya, da kuma hayin Kogin Urdun. Taro kuma ya sāke haɗuwa wurinsa, ya kuma sāke koya musu kamar yadda ya saba.

2. Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wajensa don su gwada shi, suka tambaye shi suka ce, “Halal ne mutum ya saki mata tasa?”

3. Sai ya amsa musu ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”

4. Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.”

5. Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni.