Littafi Mai Tsarki

Mar 1:9-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Sai ya zamana a wannan lokaci Yesu ya zo daga Nazarat ta ƙasar Galili. Yahaya ya yi masa baftisma a Kogin Urdun.

10. Da fitowarsa daga ruwan sai ya ga sama ta dāre, Ruhu yana sauko masa kamar kurciya.

11. Aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Kai ne Ɗana ƙaunataccena, ina farin ciki da kai ƙwarai.”

12. Nan da nan sai Ruhu ya iza shi jeji.