27. A zamanin Annabi Elisha kuma akwai kutare da yawa a Isra'ila, ba kuwa ɗayansu da aka tsarkake sai Na'aman, mutumin Suriya, kaɗai.”
28. Da suka ji haka, duk waɗanda suke a majami'a suka husata ƙwarai.
29. Sai suka tashi suka fitar da shi bayan gari, har suka kai shi goshin dutsen da aka gina garinsu a kai, don su jefa shi ƙasa.
30. Amma ya ratsa ta tsakiyarsu, ya yi tafiyarsa.
31. Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a ƙasar Galili, yana koya musu ran Asabar.
32. Suka yi mamakin koyarwarsa domin magana tasa da hakikancewa take.