Littafi Mai Tsarki

Luk 24:27-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Sai ya fara ta kan littattafan Musa da na dukan annabawa, ya yi ta bayyana musu abubuwan da suka shafe shi a dukan Littattafai.

28. Sai suka kusato ƙauyen da za su. Ya yi kamar zai ci gaba,

29. suka matsa masa suka ce, “Sauka a wurinmu, ai, magariba ta doso, rana duk ta tafi.” Sai ya sauka a wurinsu.

30. Sa'ad da yake cin abinci tare da su, sai ya ɗauki gurasa, ya yi wa Allah godiya, ya gutsura, ya ba su.

31. Idonsu ya buɗe, suka kuma gane shi. Sai ya ɓace musu.

32. Suka ce wa juna, “Ashe, zuciyarmu ba ta yi annuri ba, sa'ad da yake a hanya, yana bayyana mana Littattafai?”