Littafi Mai Tsarki

Luk 10:5-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Duk gidan da kuka sauka, ku fara da cewa, ‘Salama alaikun mutanen gidan nan!’

6. In akwai da ɗan salama a gidan, to, salamarku za ta tabbata a gare shi. In kuwa babu, za ta komo muku.

7. Ku zauna a gidan, kuna ci kuna shan duk irin abin da suka ba ku, domin ma'aikaci ya cancanci ladansa. Kada ku riƙa sāke masauki.

8. Duk garin da kuka shiga, in an yi na'am da ku, ku ci duk irin abin da aka kawo muku.

9. Ku warkar da marasa lafiya da suke cikinsa, ku kuma ce musu, ‘Mulkin Allah ya kusato ku.’