Littafi Mai Tsarki

L. Fir 22:28-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Ba za ku yanka uwar dabbar tare da ɗanta rana ɗaya ba, ko uwar saniya ce, ko ta tunkiya ce.

29. Sa'ad da za ku miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, sai ku miƙa ta yadda za a karɓa.

30. A ranar ce za a cinye, kada a bar kome ya kai gobe. Ni ne Ubangiji.

31. “Ku yi biyayya da umarnina. Ni ne Ubangiji.

32. Kada ku jawo wa sunana mai tsarki ƙasƙanci, amma sai mutanen Isra'ila su gane, ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji na kuwa tsarkake ku,

33. na kuma fisshe ku daga ƙasar Masar domin in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”