1. Ubangiji kuma ya ce wa Musa
2. ya faɗa wa mutanen Isra'ila cewa, “Ni ne Ubangiji Allahnku.
3. Kada ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan'ana inda nake kai ku. Kada ku kiyaye dokokinsu.
4. Amma ku bi ka'idodina, ku yi tafiya a cikinsu, gama ni ne Ubangiji Allahnku.
5. Domin haka sai ku kiyaye dokokina da ka'idodina waɗanda ta wurin kiyaye su mutum zai rayu. Ni ne Ubangiji.”