Littafi Mai Tsarki

L. Fir 18:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji kuma ya ce wa Musa

2. ya faɗa wa mutanen Isra'ila cewa, “Ni ne Ubangiji Allahnku.

3. Kada ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan'ana inda nake kai ku. Kada ku kiyaye dokokinsu.

4. Amma ku bi ka'idodina, ku yi tafiya a cikinsu, gama ni ne Ubangiji Allahnku.

5. Domin haka sai ku kiyaye dokokina da ka'idodina waɗanda ta wurin kiyaye su mutum zai rayu. Ni ne Ubangiji.”