Littafi Mai Tsarki

L. Fir 14:29-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Sauran man da yake cikin tafin hannunsa zai zuba a bisa wanda ake tsarkakewar, ya yi kafara dominsa a gaban Ubangiji.

30. Sai mutumin ya ba da kurciyoyi, ko 'yan tattabarai yadda ya iya,

31. ɗaya domin hadaya don zunubi, ɗaya kuma don hadaya ta ƙonawa tare da hadaya ta gari. Firist ɗin kuma zai yi kafara a gaban Ubangiji domin wanda ake tsarkakewar.

32. Wannan ita ce doka a kan mai ciwon kuturta wanda ba shi da isasshen abin bayarwa don yin hadayun tsarkakewarsa.

33. Sai kuma Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,

34. “Sa'ad da kuka shiga ƙasar Kan'ana wadda nake ba ku ku mallaka, zan sa kuturta ta yaɗu a gidajenku.” Sa'an nan Ubangiji ya ba su waɗannan ka'idodi.

35. Mutumin da ya ga kuturta a gidansa, tilas ya je ya faɗa wa firist.