Littafi Mai Tsarki

K. Mag 8:17-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata,Dukan wanda yake nemana kuma zai same ni.

18. Ina da dukiya da daraja da zan bayar,Da wadata da nasara kuma.

19. Abin da za ka samu daga gare niYa fi zinariya kyau, da azurfa tsantsa.

20. A kan hanyar adalci nake tafiya,Rankai a kan hanyoyin gaskiya.

21. Ina ba da dukiya ga waɗanda suke ƙaunata,Ina kuma cika gidajensu da wadata.

22. “Ni ce halittar farko da UbangijiYa fara halittawa daga cikin ayyukansa tuntuni.

23. Da farkon farawa ni aka fara halittawaKafin a yi duniya.