Littafi Mai Tsarki

K. Mag 11:20-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Ubangiji yana ƙin masu muguwar niyya, amma yana murna da waɗanda suke aikata abin da yake daidai!

21. Ka tabbata fa za a hukunta mugaye, amma ba za a hukunta adalai ba.

22. Kome kyan mace idan ba ta da kangado, tana kamar zoben zinariya a hancin alade.

23. Abin da mutanen kirki suke so kullum yakan jawo alheri, idan mugaye sun sami biyan bukatarsu kowa zai yi ɓacin rai.

24. Waɗansu mutane sukan kashe kuɗinsu hannu sake, duk da haka arzikinsu sai ƙaruwa yake yi. Waɗansu kuwa saboda yawan tsumulmularsu sukan talauce.

25. Ka yi alheri za ka arzuta. Ka taimaki waɗansu, su kuma za su taimake ka.

26. Mutane sukan la'anci mai ɓoye hatsi, yana jira ya yi tsada, amma sukan yabi wanda yake sayar da nasa.