Littafi Mai Tsarki

Ayu 7:7-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. “Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai,Farin cikina ya riga ya ƙare.

8. Kuna ganina yanzu, amma ba za ku sāke ganina ba.Idan kuka neme ni, za ku tarar ba na nan.

9. Kamar girgijen da yake bajewa ya tafi,Haka nan mutum yake mutuwa.

10. Ba kuwa zai ƙara komowa ba,Mutanen da suka san shi, duka za su manta da shi.

11. A'a, ko kaɗan ba zan yi shiru ba!Haushi nake ji, zuciyata ta ɓaci,Dole ne in yi magana.

12. “Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi?Kana tsammani ni dodon ruwa ne?

13. Na kwanta ina ƙoƙari in huta,Ina neman taimako don azabar da nake sha.

14. Amma kai kana firgita ni da mafarkai,Kana aiko mini da wahayi da ganegane,

15. Har nakan fi so a rataye ni,Gara in mutu da in rayu a wannan hali.

16. Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa.Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma'ana.

17. “Ya Ubangiji, me ya sa mutum yake da daraja haka a gare ka?Me ya sa kake lura da abin da yake yi?

18. Kakan dube shi kowace safiya.Kana jarraba shi a kowane daƙiƙa.

19. Ba za ka ko ɗan kawar da kai ba,Don in samu in haɗiye yau?