Littafi Mai Tsarki

Ayu 7:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. “Ya Ubangiji, me ya sa mutum yake da daraja haka a gare ka?Me ya sa kake lura da abin da yake yi?

18. Kakan dube shi kowace safiya.Kana jarraba shi a kowane daƙiƙa.

19. Ba za ka ko ɗan kawar da kai ba,Don in samu in haɗiye yau?

20. Ko na yi zunubi ina ruwanka,Kai mai ɗaure mutane?Me ya sa ka maishe ni abin bārata?Ni wani babban kaya mai nauyi ne a gare ka?

21. Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba?Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba?Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura,Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”