Littafi Mai Tsarki

Ayu 7:10-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ba kuwa zai ƙara komowa ba,Mutanen da suka san shi, duka za su manta da shi.

11. A'a, ko kaɗan ba zan yi shiru ba!Haushi nake ji, zuciyata ta ɓaci,Dole ne in yi magana.

12. “Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi?Kana tsammani ni dodon ruwa ne?

13. Na kwanta ina ƙoƙari in huta,Ina neman taimako don azabar da nake sha.

14. Amma kai kana firgita ni da mafarkai,Kana aiko mini da wahayi da ganegane,

15. Har nakan fi so a rataye ni,Gara in mutu da in rayu a wannan hali.

16. Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa.Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma'ana.

17. “Ya Ubangiji, me ya sa mutum yake da daraja haka a gare ka?Me ya sa kake lura da abin da yake yi?

18. Kakan dube shi kowace safiya.Kana jarraba shi a kowane daƙiƙa.

19. Ba za ka ko ɗan kawar da kai ba,Don in samu in haɗiye yau?

20. Ko na yi zunubi ina ruwanka,Kai mai ɗaure mutane?Me ya sa ka maishe ni abin bārata?Ni wani babban kaya mai nauyi ne a gare ka?

21. Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba?Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba?Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura,Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”