Littafi Mai Tsarki

Ayu 42:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ayuba ya amsa wa Ubangiji.

2. “Na sani kai kake da ikon yin dukan abu,Ba wanda ya isa ya hana ka yin abin da ka nufa.

3. Wane ne wannan marar ilimi da zai ɓoye shawara?Saboda haka na hurta abin da ban gane ba,Abubuwa waɗanda ban gane ba suna banmamaki ƙwarai.

4. Ka ce, ‘Kasa kunne, zan yi magana da kai,Zan yi maka tambaya, ka ba ni amsa.’

5. Dā jin labarinka nake,Amma yanzu na gan ka ido da ido.

6. Saboda haka na ga ni ba kome ba ne,Na tuba, ina hurwa da ƙura da toka.”