Littafi Mai Tsarki

Ayu 40:6-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Sa'an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba daga cikin guguwa, ya ce,

7. “Tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji,Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa.

8. Kai kanka za ka sa mini laifi?Za ka kā da ni don kai ka barata?

9. Kana da ƙarfi kamar na Allah?Kana iya tsawa da murya kamar tasa?

10. “Ka caɓa ado da kwarjini da ɗaukaka,Ka yafa daraja da maƙami.

11. Ka kwararar da rigyawar fushinka,Ka dubi dukan wanda yake alfarma, a wulakance.