Littafi Mai Tsarki

Ayu 39:12-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Ka gaskata zai komo,Ya kawo maka hatsi a masussukarka?

13. “Jimina takan karkaɗa fikafikanta da alfarma!Amma ba su ne gashin fikafikan ƙauna ba.

14. Jimina takan bar wa ƙasa ƙwayayenta,Ta bar ƙasa ta ɗumama su.

15. Takan manta wani ya iya taka su su fashe,Ya yiwu kuma wani naman jeji ya tattake su.

16. Takan yi wa 'ya'yanta mugunta,Sai ka ce ba nata ba ne,Ko da yake ta sha wahala a banza,Duk da haka ba ta damu ba.

17. Gama Allah bai ba ta hikima ba,Bai kuwa ba ta fahimi ba.

18. Amma sa'ad da ta sheƙa a guje,Takan yi wa doki maguji da mahayinsa dariya.

19. “Kai ka yi wa doki ƙarfinsa?Kai ne kuma ka daje wuyansa da geza?

20. Kai ne ka sa shi tsalle kamar ɗango?Kwarjinin firjinsa yana da bantsoro.

21. Yakan yi nishi a fadama,Yana murna saboda ƙarfinsa,A wurin yaƙi ba ya ja da baya, ba ya jin tsoron kibau.

22. Tsoro abin dariya ne a gare shi, bai damu ba.Ba ya ba da baya ga takobi,