Littafi Mai Tsarki

Ayu 35:12-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Suka yi kira don taimako, amma Allah bai amsa ba,Saboda suna da girmankan mugaye.

13. Hakika Allah bai ji holoƙon kukansu ba,Allah Mai Iko Dukka kuwa bai kula da shi ba.

14. “Ayuba, kai wane ne da za ka ce ba ka gan shi ba?Da kake cewa ƙararka tana gabansa,Jiransa kake yi?

15. Yanzu fa saboda bai yi hukunci da fushinsa ba,Kamar kuma bai kula da laifi ba,

16. Ayuba, maganarka marar ma'ana ce,Ka yi ta maganganu marasa hikima.”