Littafi Mai Tsarki

Ayu 30:9-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. “Yanzu na zama abin waƙa gare su,Abin ba'a kuma a gare su.

10. Suna ƙyamata, guduna suke yi,Da ganina, sai su tofa mini yau.

11. Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni,Saboda haka sun raba ni da zuriyata,

12. A hannun dama 'yan tā da zaune tsaye sun taso mini,Sun runtume ni, sun tura ni a hanyarsu ta hallakarwa.

13. Sun datse hanyata,Sun jawo mini bala'i,Ba kuwa wanda ya hana su.

14. Sun kutsa kamar waɗanda suka karya doka,Sun auka mini da dukan ƙarfinsu kamar yadda suka yi nufi.

15. Sun firgita ni,Sun kori darajata kamar da iska,Wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije.

16. “Yanzu zuciyata ta narkeKwanakin wahala sun same ni.