6. Sai a kwazazzabai suke zamaDa a ramummuka da kogwannin duwatsu.
7. Suka yi ta kuka a jeji,Suka taru wuri ɗaya a cikin sarƙaƙƙiya.
8. Mutane ne marasa hankali marasa suna!Aka kore su daga ƙasar.
9. “Yanzu na zama abin waƙa gare su,Abin ba'a kuma a gare su.
10. Suna ƙyamata, guduna suke yi,Da ganina, sai su tofa mini yau.
11. Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni,Saboda haka sun raba ni da zuriyata,