Littafi Mai Tsarki

Ayu 22:19-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Mutanen kirki suna murna,Marasa laifi kuma suna dariyaSa'ad da suka ga ana hukunta mugaye.

20. Duk abin da mugu ya mallaka ya hallaka,Wuta kuwa ta lashe kowane abu da ya ragu.

21. “Yanzu fa, Ayuba, sai ka yi sulhu da Allah,Ka daina ɗaukarsa kamar maƙiyinka,In ka yi haka, to, za ka sami albarka.

22. Ka karɓi koyarwar da yake yi,Ka riƙe kalmominsa a zuciyarka.

23. Hakika sai ka yi tawali'u, ka koma wurin Allah,Ka kawar da dukan muguntar da ake yi a gidanka.

24. Ka jefar da zinariyarka, zinariyarka mafi kyau,Ka jefar da ita kamar dutse ko ƙura.