Littafi Mai Tsarki

Ayu 15:11-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. “Allah yana ta'azantar da kai,Me ya sa har yanzu ka ƙi kulawa da shi?Mun yi magana a madadinsa a natse da lafazi mai daɗi.

12. Amma ka ta da hankalinka,Kana ta zazzare mana ido da fushi.

13. Fushi kake yi da Allah, kana ƙinsa.

14. Akwai mutumin da yake tsarkakakke sarai?Akwai mutumin da yake cikakke a wurin Allah?

15. Me ya sa Allah bai sakar wa mala'ikunsa kome ba?Har su ma ba tsarkaka suke a gare shi ba.

16. Mutum yakan sha mugunta kamar yadda yake shan ruwa,Hakika mutum ya lalace, ya zama mai rainako.

17. “Yanzu ka saurara, ya Ayuba, ga abin da na sani.

18. Mutane masu hikima sun koya mini gaskiyaWadda suka koya daga wurin kakanninsu,Ba su kuwa ɓoye mini asirin kome ba.

19. Ƙasaru 'yantacciya ce daga baƙiBa wanda zai raba su da Allah.

20. “Mugun mutum mai zaluntar sauran mutaneZai kasance da wahala muddin ransa.

21. Zai ji ƙarar muryoyi masu firgitarwa a kunnuwansa.'Yan fashi za su fāɗa masaSa'ad da yake tsammani ba abin da zai same shi.

22. Bai sa zuciya zai kuɓuta daga duhu ba,Gama takobi yana jiransa a wani wuri don ya kashe shi.

23. Yana ta yawon neman abinci, yana ta cewa, ‘Ina yake?’Ya sani baƙin ciki ne yake jiransa a nan gaba. Kamar sarki mai iko,