Littafi Mai Tsarki

A.m. 7:46-49 Littafi Mai Tsarki (HAU)

46. wanda ya sami tagomashi wurin Allah, har ya nemi alfarmar yi wa Allahn Yakubu masujada.

47. Amma Sulemanu ne ya yi wa Allah gini.

48. Duk da haka Maɗaukaki ba ya zama a gidaje, ginin mutum. Yadda Annabi Ishaya ya ce,

49. ‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina,Ƙasa kuwa matashin ƙafata.Wane wuri kuma za ku gina mini?Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna?