Littafi Mai Tsarki

A.m. 4:32-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. To, duk taron da suka ba da gaskiya kuwa nufinsu ɗaya ne, ra'ayinsu ɗaya, ba kuma waninsu da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, sai dai kome nasu ne baki ɗaya.

33. Manzanni kuma suka yi shaida da tabbatarwa mai ƙarfi a kan tashin Ubangiji Yesu daga matattu. Alheri mai yawa yana tare da kowannensu,

34. har ba wanda yake da rashi a cikinsu ko ɗaya, don duk masu gonaki ko gidaje sun sayar da su,

35. sun kawo kuɗin, sun ajiye gaban manzanni, an kuwa rarraba wa kowa gwargwadon bukatarsa.

36. Ana cikin haka sai Yusufu, wani Balawiye, asalinsa mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannin suke kira Barnaba, (wato ɗan ƙarfafa zuciya),

37. ya sayar da wata gonarsa, ya kawo kuɗin ya ajiye a gaban manzannin.