Littafi Mai Tsarki

A.m. 28:28-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. To, sai ku sani, wannan ceto na Allah, an aiko da shi har ga al'ummai, su kam za su saurara.”

29. (Da ya faɗi haka, sai Yahudawa suka tashi suna ta muhawwara da juna.)

30. Sai Bulus ya zauna a nan a gidan da yake haya, har shekara biyu cikakku, yana maraba da duk wanda ya je wurinsa,

31. yana ta wa'azin Mulkin Allah, da koyar da al'amarin Ubangiji Yesu Almasihu gabagaɗi, ba tare da wani hani ba.