Littafi Mai Tsarki

A.m. 2:5-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. To, a Urushalima a lokacin, akwai waɗansu Yahudawa masu bautar Allah daga ko'ina cikin ƙasashen duniya.

6. Da jin dirin nan kuwa, taron ya haɗe, ya ruɗe, domin ko wannensu ya ji suna magana da bakin garinsu.

7. Sai suka yi al'ajabi suka yi mamaki, suna cewa, “Ashe, duk masu maganar nan ba Galilawa ba ne?

8. Ƙaƙa kuwa ko wannenmu yake ji da bakin garinsu ake magana?

9. Ga mu kuwa, Fartiyawa, da Madayanawa, da Elamawa, da mutanen ƙasar Bagadaza, da na Yahudiya, da na Kafadokiya, da na Fantas, da na Asiya,