Littafi Mai Tsarki

A.m. 2:20-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Za a mai da rana duhu,Wata kuma jini,Kafin Ranar Ubangiji ta zo,Babbar ranar nan mai girma.

21. A sa'an nan ne zai zamanto kowa ya yi addu'a da sunan Ubangiji zai sami ceto.’

22. “Ya ku 'yan'uwa, Isra'ilawa, ku ji wannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar muku cewa shi yardajjensa ne, ta mu'ujizai, da abubuwan al'ajabi, da alamu waɗanda ya yi ta wurinsa a cikinku, kamar yadda ku kanku kuka sani,

23. shi Yesun nan fa, an ba da shi bisa ƙaddarar Allah da rigyasaninsa, ku kuwa kuka gicciye shi, kuka kashe shi, ta hannun masu zunubi.

24. Amma Allah ya tashe shi bayan ya ɓalle masa ƙangin mutuwa, domin ba shi yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.

25. Dawuda kuma ya yi faɗi a game da shi ya ce,‘Kullum hankalina yana kan Ubangiji,Yana damana, domin kada in jijjigu.

26. Saboda haka, zuciyata ta yi fari, ina farin ciki matuƙa.Ko da yake kuma ni jiki ne, zan zauna ina sa zuciya,

27. Domin ba za ka yar da raina a Hades ba,Ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.

28. Kā sanar da ni hanyoyin rai.Za ka cika ni da farin ciki ta zamana a zatinka.’