Littafi Mai Tsarki

A.m. 16:32-40 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Sa'an nan suka gaya masa Maganar Ubangiji, shi da iyalinsa duka.

33. Nan take da daddaren nan ya ɗebe su, ya wanke musu raunukansu. Nan da nan kuwa aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.

34. Sa'an nan ya kawo su gidansa, ya kawo musu abinci, ya yi ta farin ciki matuƙa, domin shi da iyalinsa duka sun gaskata da Allah.

35. Amma da gari ya waye, sai alƙalan suka aiko dogarai, suka ce, “Suka ce a saki mutanen nan.”

36. Yari kuwa ya shaida wa Bulus maganar, ya ce, “Alƙalai sun aiko a sake ku, saboda haka yanzu sai ku fito, ku tafi lafiya.”

37. Amma Bulus ya ce musu, “Ai, a fili suka daddoke mu, ba ko bin ba'asi, mu ma da muke Romawa bisa ga 'yangaranci, suka jefa mu a kurkuku, yanzu kuma sā fitar da mu a ɓoye? Sai dai su zo da kansu su fito da mu.”

38. Sai dogarai suka shaida wa alƙalan wannan magana. Su kuwa da suka ji Bulus da Sila Romawa ne suka tsorata.

39. Sa'an nan suka zo suka tubar musu, bayan kuma sun fito da su, suka roƙe su su bar garin.

40. To, da suka fita daga kurkukun, suka tafi wurin Lidiya. Bayan sun ga 'yan'uwa, suka kuma ƙarfafa musu zuciya, suka tashi.