Littafi Mai Tsarki

A.m. 16:31-34 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. Su kuwa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”

32. Sa'an nan suka gaya masa Maganar Ubangiji, shi da iyalinsa duka.

33. Nan take da daddaren nan ya ɗebe su, ya wanke musu raunukansu. Nan da nan kuwa aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.

34. Sa'an nan ya kawo su gidansa, ya kawo musu abinci, ya yi ta farin ciki matuƙa, domin shi da iyalinsa duka sun gaskata da Allah.