Littafi Mai Tsarki

A.m. 13:35-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

35. Domin a wata Zabura ma ya ce,‘Ba za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.’

36. Dawuda kam, bayan da ya bauta wa mutanen zamaninsa bisa ga nufin Allah, ya yi barci, aka binne shi tare da kakanninsa, ya kuwa ruɓe.

37. Amma shi wannan da Allah ya tashe shi, bai ruɓa ba.

38. Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku sani albarkacin mutumin nan ne ake sanar da ku gafarar zunubanku.

39. Ta gare shi kuma, duk masu ba da gaskiya suka kuɓuta daga dukan abubuwan da ba dama Shari'ar Musa ta kuɓutar da ku.

40. Saboda haka sai ku mai da hankali, kada abin nan da littattafan annabawa suke faɗa ya aukar muku, wato

41. ‘Ga shi, ku masu rainako,Za ku ruɗe don mamaki, ku shuɗe!Domin zan yi wani aiki a zamaninku,Aikin da ba yadda za a yi ku gaskata,Ko da wani ya gaya muku.’ ”

42. Suna fita majami'a ke nan, sai mutane suka roƙe su su ƙara yi musu wannan magana a ran Asabar mai zuwa.

43. Da jama'a suka watse, Yahudawa da yawa, da kuma waɗanda suka shiga Yahudanci, masu ibada, suka bi Bulus da Barnaba. Su kuma suka yi musu magana, suna yi musu gargaɗi su zauna a cikin alherin Allah.