Littafi Mai Tsarki

Afi 6:8-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Kun sani, kowane alherin da mutum ya yi, ko shi ɗa ne ko bawa, Ubangiji zai sāka masa shi.

9. Ku iyayengiji, ku ma ku yi musu haka, ku bar tsorata su, ku sani, shi wanda yake Ubangijinsu da ku duka, yana Sama, shi kuwa ba ya zaɓe.

10. A ƙarshe kuma, ku ƙarfafa ga Ubangiji, ga ƙarfin ikonsa.

11. Ku yi ɗamara da dukan makamai na Allah, don ku iya dagewa gāba da kissoshin Iblis.

12. Ai, famarmu ba da 'yan adam muke yi ba, amma da mugayen ruhohi ne na sararin sama, masarauta, masu iko, da waɗanda ragamar mulkin zamanin nan mai duhu take hannunsu.

13. Saboda haka, sai ku ɗauki dukan makamai na Allah, domin ku iya dagewa a muguwar ranar nan, bayan kuma kun gama kome duka, ku dage.

14. Saboda haka fa ku dage, gaskiya ta zama ɗamararku, adalci ya zama sulkenku,

15. shirin kai bisharar salama ya zama kamar takalmi a ƙafafunku.

16. Banda waɗannan kuma, ku ɗauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku iya kashe dukan kiban wutar Mugun nan da ita.

17. Ku kuma ɗauki kwalkwalin ceto, da takobin Ruhu, wato Maganar Allah,

18. a koyaushe kuna addu'a da roƙo ta wurin ikon Ruhu ba fāsawa. A kan wannan manufa ku tsaya da kaifinku da matuƙar naci, kuna yi wa dukan tsarkaka addu'a.